ABNA24 : A wata sanarwa da ya fitar, Gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya ce dokar za ta fara aiki daga ƙarfe 4 na yammacin yau Talata inda ya ce dokar ta hana kowa fitowa kan tituna face masu ayyukan hidima da ya zama wajibi su kasance a bisa tituna.
Gwamnan ya ce, ya shiga damuwa yadda ya ga zanga-zangar lumana ta #EndSARS ta rikiɗe ta zama wani abin ban tsoro da ke barazana ga zaman lafiyar al'umma saboda yadda bata-gari suka fake da sunan zanga-zangar suna kashe mutane don haka ya ce ba za su taba bari jihar ta Lagos ta zama tamkar fagen yaki ba.
Rahotanni daga sassan daban-daban na Lagos ɗin na nuni da cewa a al’amura na daɗa taɓarɓarewa sakamakon yadda wasu ɓata garin ke kaiwa jama’a hari da kwace musu kayayyaki, bugu da kari kan sanya wuta a kan dukiyoyin al’umma.
Gwamnatin jihar Edo ce fara ta sanya dokar hana fita bayan wasu 'yan daba da ɓata gari da suka fake da zanga-zangar #endsars ɗin suka kai hari wasu gidajen yari biyu da kuma sake fursunonin da suke ciki bayan kona wasu ofisoshin ‘yan sanda da suka yi.
A babban birnin Tarayyar Nijeriya ɗin ma dai Abuja, an samu irin wannan tarzomar inda ɓata garin suka ci gaba da cin zarafin mutane da kuma ƙone-ƙone lamarin da ya sanya aka fara kiran gwamnatin da ta ɗau matakan da suka dace wajen kare lafiya da dukiyar al’umma.
342/